TAMBAYA

Shin ya halatta ga Musulmi ya ci  abincin da kiristoci  ko wanda ba musulba suka shirya a ranakun bukukuwan su(kirsimeti), ko ya karɓi kyauta daga gare su saboda tayasu murnar bukukuwan su?


AMSA

1-Sharaa ta halattawa musulmi cin abincin kiristoci ko amsar kyauta daga garesu  haka kaima an halattama kabasu abinci ko kayi musa kyauta ko muamalattarsu ko kasuwanci tare dasu abisa tsari na musulunci, amma gameda cin abincinsu ko amsar kyautuka daga garesu lokutan bukukuwansu na Ibada ga fatawar malamai daga LAJNATUD DAIMA

2- “Ba ya halatta ga Musulmi ya ci daga cikin abincin da Yahudawa ko Nasara ko mushrikai suka shirya don bukukuwan su na Ibada, kuma ba ya halatta ga Musulmi ya karɓi kyauta daga gare su saboda bukukuwan su na Ibada. Domin yin hakan yana nuna girmamawa da tayasu murna, da kuma yin aiki tare da su wajen bayyana al'adun addininsu, tallata bid'arsu, da kuma shiga farin cikin da suke yi a ranakun bukukuwan su wanda Hakan kuma ya sabawa sharaar mususlunci.”

Saboda manzan Allah (saw) yace:( mutum yana tare da wanda yakeso Ranar Alqiyama).

A  wani hadisin kuma yace:( wanda yayi kamanceceniya da wasu mutane to yana cikinsu).

Bisa waannan dalilan yazama Haramunne tayasu ko taimakonsu akan bukukuwansu  ko ayyukan da sukashafi ibadunsu ko tayasu farin ciki a irin wannan lokaci.


Allah yasa mudace.

Muhammad Idris Kumbash

2 Comments

Post a Comment

Previous Post Next Post