Falalar Ranakun Goma na Zul-Hijja

 Falalar Ranakun Goma na Zul-Hijja


Daga cikin lokutan ibada mafi girma akwai ranakun goma na farkon watan Zul-Hijja, wadanda Allah Maɗaukaki ya fifita su akan sauran kwanakin shekara. Daga Abdullahi bn Abbas (RA), daga Annabi (SAW), ya ce: "Babu wasu kwanaki da aikin alheri ya fi soyuwa ga Allah fiye da waɗannan kwanaki" – ma’ana, kwanakin goma na Zul-Hijja. Suka ce: "Ko jihadi a tafarkin Allah ma?" Ya ce: "Ko jihadi a tafarkin Allah ma bai kai ba, sai dai mutumin da ya fita da kansa da dukiyarsa, bai dawo da komai daga ciki ba." (Bukhari 969, Abu Dawud 2438 – lafazin na Abu Dawud ne, Tirmizi 757, Ibn Majah 1727).

Waɗannan nassoshi da makamantansu suna nuna cewa wadannan ranaku goma sun fi sauran kwanakin shekara dukkaninsu, har ma da kwanakin karshe na watan Ramadan. Sai dai, dararen karshe na Ramadan sun fi dararen Zul-Hijja, domin suna dauke da daren Lailatul Qadr, wanda ya fi daren watanni dubu. Duba Tafsirin Ibn Kathir 5/412.


Ayyukan Da Ake So a Yi a Ranakun Goma na Zul-Hijja

Ya kamata Musulmi ya fara wadannan ranaku da tuba ta gaskiya zuwa ga Allah (SWT), sannan ya yawaita yin ayyukan alheri gaba ɗaya. Amma wadannan ayyuka da ke biye sun fi cancanta a kula da su:


1. Azumi

Sunnace ga Musulmi ya yi azumin kwanaki tara na farkon Zul-Hijja. Domin Annabi (SAW) ya karfafa yin aikin alheri a cikin wadannan kwanaki, kuma azumi na daga cikin mafi girman ayyuka. A cikin hadisin Qudsi: "Dukkan aikin ɗan Adam na shi ne, sai dai azumi, domin shi nawa ne, ni ne zan ba da lada." (Bukhari 1805).

An ruwaito cewa Annabi (SAW) yana azumin kwanaki tara na Zul-Hijja, da ranar Ashura, da kuma kwana uku a kowane wata – Litinin na farko da Alhamis biyu. (Nasa’i 4/205, Abu Dawud, Albani ya sahihanta a Sahih Abi Dawud 2/462).


2. Yawaita Tahmeed, Tahleel, da Takbeer

Sunnace a yawaita takbiri, tahmeedi, tahleeli, da tasbihi a cikin wadannan kwanaki. A bayyana a cikin masallatai, gidaje, tituna, da duk inda aka yarda a ambaci Allah. Maza su bayyana shi da murya, mata su yi shi cikin sirri.

Allah ya ce:

"Su shaida amfanin da ke gare su, kuma su ambaci sunan Allah a ranakun da aka sani bisa abin da Ya azurta su daga dabbobin hadaya." (Suratul Hajj: 28). Mafi yawan malamai sun fassara "ayyamin ma’lumat" a matsayin ranakun goma na Zul-Hijja kamar yadda Ibn Abbas (RA) ya fassara.

Daga Abdullah bn Umar (RA), daga Annabi (SAW):

"Babu wasu kwanaki mafi girma wajen Allah kuma mafi soyuwa ayyuka a cikinsu fiye da wadannan kwanakin goma. Don haka ku yawaita tahleel, takbeer, da tahmeed a cikinsu." (Ahmad 7/224 – Ahmad Shakir ya inganta sanadinsa).


Siffofin Takbiri sun hada da:

"Allahu Akbar, Allahu Akbar, Laa ilaaha illallaah, Wallahu Akbar, Allahu Akbar wa lillaahil hamd." Kuma akwai wasu siffofi daban.

Yin takbiri a wannan zamani ya zama abin da mutane suka yi watsi da shi, musamman a farkon ranakun goma, inda ba ka jin shi sai daga 'yan kadan. Don haka, ya dace a bayyana shi don farfado da sunnah da tunatar da masu mantuwa.

An tabbatar cewa Ibn Umar da Abu Huraira (RA) suna fita kasuwa a ranakun goma suna takbiri, sai mutane su karɓi takbirinsu – ba da hadin baki ko da sauti ɗaya ba, domin hakan ba sunnah ba ne.

Farfado da sunnah da aka manta yana da lada mai yawa kamar yadda Annabi (SAW) ya ce:

"Wanda ya farfado da wata sunnata da aka manta bayan ni, to yana da lada kamar wanda ya aikata ta ba tare da rage musu ladansu ba." (Tirmizi 7/443 – hadisi mai kyau ne bisa shaidu).


3. Yin Hajji da Umrah

Daya daga cikin mafi girman ayyuka a cikin wadannan kwanaki shine yin Hajji zuwa Dakin Allah. Duk wanda Allah ya bashi sa’a ya je Hajji ya kuma cika shi yadda ya dace, yana da wani kaso daga hadisin Annabi (SAW):

"Hajjin da aka karɓa ba shi da lada sai Aljanna."


4. Hadaya

Daga cikin ayyukan alheri a cikin wadannan kwanaki akwai kusar  Allah ta hanyar yanka hadaya. A zabi mai kyau kuma lafiyayye daga cikin dabbobi da yin kyauta wajen kashe kudi domin Allah.

Mu gaggauta amfani da wadannan kwanaki masu falala, kafin wanda ya yi sakaci ya yi nadama, ko kuma ya roki dawowa amma ba a amsa masa ba.

Allah yasa mudace


Muhammad Idris kumbash

Post a Comment

Previous Post Next Post